News
Rasha ta kai hari tashar jiragen ruwan Ukraine
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.
Gwamnan yankin Odesa na Ukraine Oleh Kiper ya ce mutum guda ya mutu, sannan akalla mtum 15 sun jikkata, sakamakon harin da jiragen saman Rasha suka kai a tashar jirgin ruwa da ke yankin odesa na ukaine.
Ya ƙara da cewa harin ya kuma haifar da lalacewar ababen more rayuwa na fararen hula, da gine-ginen jama’a da kuma wata coci.
Gwamnatin jihar Filato ta musanta cewa sama da shanu 1,000 ne suka mutu sakamakon wata bakuwar cuta
Birnin Odesa na fuskantar hare-hare a baya-bayan nan daga dakarun Rasha, tun bayan sanarwar da Moscow ta bayar a makon da ya gabata cewa ba za ta sabunta yarjejeniyar fitar da hatsi ba.
Tashar ruwa ta Odesa, ita ce tasha ra jiragen ruwa mafi girma a Ukraien, kuma an yi jigilar miliyoyin tan na hatsi daga tashar a ƙarƙashin yarjejeniyar da Turkiyya ta jagoranci ƙullawa
