News
Tinubu ya gana da gwamnonin jihohin da ke da iyaka da Jamhuriyar Nijar.
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya gana da gwamnonin jihohin da ke da iyaka da Jamhuriyar Nijar.
Taron dai wani bangare ne na tuntubar shugaban kasar kan halin da ake ciki a Nijar.
Gwamnonin da suka gana da shugaban a Aso Rock sun hada da Ahmed Aliyu (Sokoto), Umar Namadi (Jigawa), Mai Mala Buni (Yobe), Idris Nasir (Kebbi) da Dr Dikko Radda (Katsina).
Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS karkashin jagorancin Tinubu ta yi barazanar daukar matakin soji kan kasar Nijar, matakin da aka ki amincewa da shi a Najeriya.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days agoGwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
