News
Gwamnatin jahar Kano Ta Kaddamar Da Kwamitin Tantance Ma’aikata Kusan Dubu 10 da 800
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.
Gwamnatin jihar Kano ta kafa kwamitin mutum 22 domin tantance ma’aikata kusan dubu 10 da 800 da aka dauka aiki a karshen wa’adin gwamnatin da ta gabata ta Dr. Abdullahi Umar Ganduje.
Sakataren gwamnatin jihar Kano, Dr. Baffa Bichi, ya ce kwamitin zai tabbatar da ko anbi ka’ida wajen daukar ma’aikata kusan dubu 10 da 800.
Gwamnatin Kano Ta Bayyana Damuwa Kan Yunkurin Bada Cin Hanci A Kotun Kararrakin Zabe
Kwamitin zai yi aiki bisa jagorancin shugaban hukumar daukar ma’aikata, Alhaji Umar Shehu Minjibir, kuma an baiwa kwamitin wa’adin makonni uku ya kammala aikinsa.
A martanin da ya mayar, Minjibir ya yi alkawarin cewa mambobin kwamitin za su yi iya kokarinsu don ganin sun kammala aikin a kan lokaci.
-
News1 day ago
Jam’iyyar Labour Party Ta Yi Alkawarin Kafa Hukumar Kula Da Hayar Gidaje A Kano
-
News3 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News6 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
