News
Wata Mata Ta Kashe Dan Kishiyarta Dan Kimanin Kwanaki Hudu A Duniya A Bauchi
DAGA AISHA MUHAMMAD
Wata mata mai suna Furera Abubakar mai shekaru 24 a duniya ta kashe dan kishiyarta dan kimanin kwanaki hudu a duniya a kauyen Bantu dake cikin karamar hukumar Ningi ta jihar Bauchi.
Kakakin rundunar ‘Yan sanda a jihar SP Ahmed Wakil shi ne ya tabbatar da kama wacce ake zargin cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya Talata.
Wakil, yayi bayanin cewa an kai rahoton faruwar lamarin zuwa ofishin yan sanda dake Ningi a ranar 19 ga watan Augusta 2023, kwanaki bayan haihuwar jaririn.
SP Wakili, ya kara da cewa yanzu haka ana cigaba da gudanar da bincike inda daga bisani za a gurfanar da wacce ake zargin a gaban kotu.
-
Opinion5 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion5 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News3 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
