Connect with us

News

Gwamnan Ondo Ya Dawo bayan shafe kimanin wata uku yana jinya a kasar Jamu

Published

on

Gwamnan Jihar Ondo, Rotimi Akeredolu

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Gwamnan Jihar Ondo, Rotimi Akeredolu, ya dawo Jihar bayan shafe kimanin wata uku yana jinya a kasar Jamus.

Bayanai sun nuna tuni mukarraban gwamnatin suka isa Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, domin su tarbe shi.

Gwamnatin Jiha Ta Bada Umarnin Rufe Kwalejin Fasaha 

Tun a watan Yuni ne dai Gwamnan ya tafi hutun neman lafiya na wata daya, kafin daga bisani ya nemi Majalisar Dokokin Jihar da ta tsawaita masa shi.

A lokacin dai ya mika ragamar mulkin Jihar a hannun mataimakinsa, Lucky Aiyedatiwa, kamar yadda Kundin Tsarin Mulki ya bukata.

Advertisement

Hotuna da bidiyon Gwamnan dai a wani asibiti a kasar Jamus lokacin da yake bikin cika shekara 67 da haihuwa.

A cikin bidiyon, an ga Gwamnan yana tikar rawa tare da matarsa da kuma wasu abokansa.

Wata majiya ta ce Gwamnan zai isa Ibadan inda zai huta na ’yan kwanaki kafin ya wuce Jihar ta Ondo.

Gwamnatin Jiha Ta Bada Umarnin Rufe Kwalejin Fasaha 

Wani labarin kuma Rashin wutar lantarki da ake fama dashi tun kafin yanzu ya kara tsananta jiya a nan Jihar Kano, A yayin da kanfanin rarraba hasken wutar lantarki na KEDCO ya tsayar da aiyukansa kacokan, Lamarin da ya haifar da daukewar lantarki baki daya a cikin birnin Kano.

Wata sanarwa da shugaban sashin sadarwar kanfanin, Sani Bala Sani ya fitar, Ya alakanta daukewar wutar lantarkin da yin biyayya ga umarnin kungiyar kwadago ta kasa na tafiya yajin aikin gargadi na tsawon kwanaki biyu.

Advertisement

Sanarwar da aka wallafa a shafin X na kanfanin, Ta baiyana cewar za’a cigaba da fuskantar matsalar daukewar wutar lantarkin, kasancewar yajin aikin gargadin zai ci gaba da kasancewa a yau Laraba.

Shima mataimakin shugaban kungiyar kwadago ta kasa reshen jihar Kano, Kwamared Ado Riruwai, ya tabbatar da cewar kungiyarsu ta rufe dukkanin wasu ofisoshin gwamnati dake jihar Kano, domin tabbatar da yajin aikin gargadin.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending