Connect with us

News

Rukunin farko na dakarun Faransa sun fara ficewa daga Jamhuriyar Nijar

Published

on

Dakarun Faransa suka fara janyewa daga Jamhuriyar Nijar

DAAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

Advertisement

A jiya Alhamis, dakarun Faransa suka fara janyewa daga Jamhuriyar Nijar, kamar dai yadda shugaba Emmanuel Macron ya alƙawarta a ranar 24 ga watan Satumbar da ya gabata.

Sojojin Faransa na farko da suka fara ficewa a jiyan su ne dakaru 400 da ke a yankin Walam, daf da iyakar Nijar da Mali, kuma sun kasance suna aikin samar da tsaro ne ƙarƙashin wani shiri da aka yi wa take ‘Operation Almahaou’, wanda babbar manufarsa ita ce samar da tsaro a yankin Liptako.

Advertisement

Nijeriya ta shirya ƙarfafa ƙawance da ungiyar Ƙasashen Turai don yaƙi da matsalolin tsaro

Waɗannan dakaru za su isa birnin Yamai ne ta ƙasa, amma hakan na buƙatar cikakken tsari da kuma tsaro ga ayarin sojojin daga inda za su tashi har zuwa cikin birnin Yamai.

 

Advertisement

Duk da cewa tazarar ba ta wuce kilomita cari ɗaya ba, amma dakarun za su iya share tsawon yini biyu saboda rashin kyawun hanya.

Da zarar sun isa Yamai kuwa, nan take dakarun 400 za su fara tashi zuwa Faransa ta jirgin sama.

Advertisement

Rundunar sojojin Faransa dai ta ce, tana fatan gudanar da wannan aiki ne da haɗin-gwiwar mahukuntan Nijar, yayin da sojoji da suka ƙwaci mulki a ƙasar ke cewa ga alama Faransa ba ta da niyyar janye dakarunta daga ƙasar.

 

Advertisement

Wannan dai gagarumin aiki ne da ya tanadi kwashe sojoji fiye da dubu ɗaya da kuma manyan sunduƙai makare da kayan aikinsu, kuma dole sai an yi amfani da hanyoyi na ƙasa domin jigilar waɗannan kaya a cikin watanni uku.

To sai dai yayin da ake hasashen cewa za a isar da kayan ne a tashar jiragen ruwan birnin Cotonou, tuni mahukuntan sojin Nijar suka ce ba za su buɗe iyakar ƙasar ta ɓangaren jamhuriyar Benin ba.

Advertisement

A wani labarin kuma Nijeriya ta shirya ƙarfafa ƙawance da ungiyar Ƙasashen Turai don yaƙi da matsalolin tsaro

Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.

Advertisement

 

Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.

Advertisement

 

A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.

Advertisement

 

Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending