News
Cibiyar Ciyarwa Fisabilillahi ta gudanar da rabon abinci ga marayu da masu rauni a Kano.
DAGA ABDURRASHID B.IMAM
A safiyar ranar juma’a ne cibiyar mai suna ciyarwa fisabilillahi ta gudanar da rabon abinci ga marayu da masu rauni a jahar kano.
Jaridar Inda Ranka ta rawaito cewa An gudanar da rabon ne a unguwar kawo da yakasai durumin zungura a nan jahar kano
Shugabar cibiyar khadija Ahmad yusuf wadda aka fi sani da rufaida ta bayyanawa manema labarai cewar ta fara aiwatar da wanann aiki ne a ranar 29-09-2023 ana fara da rabawa marayu hamsin dafaffan abinci haka tace gudanar da hakan ne duk domin ragewa al’umma radadin matsin rayuwa
Rufaidan ta kara da cewar wannan cibiya tana samun kudin wannan ciyarwa ne daga hannu daidaikun Al’umma masu hali
Daga karshe ta bayyana hanyar da za a same ta ga masu son taimakawa za a same ta ta lambar wayar ta kira ko whatapp 07064517451
Aminu sani da zainab zakari cikin wadan da suka samu wannan abinci sun bayyana farin cikin su hadi da godewa Allah da wannan cibiya tare da addu’ar Allah ya kara daga wannan cibiya
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
