Connect with us

News

Cibiyar Ciyarwa Fisabilillahi ta gudanar da rabon abinci ga marayu da masu rauni a Kano.

Published

on

khadija Ahmad yusuf

DAGA ABDURRASHID B.IMAM

 

A safiyar ranar juma’a ne cibiyar mai suna ciyarwa fisabilillahi ta gudanar da rabon abinci ga marayu da masu rauni a jahar kano.

Jaridar Inda Ranka ta rawaito cewa An gudanar da rabon ne a unguwar kawo da yakasai durumin zungura a nan jahar kano

 

Shugabar cibiyar khadija Ahmad yusuf wadda aka fi sani da rufaida ta bayyanawa manema labarai cewar ta fara aiwatar da wanann aiki ne a ranar 29-09-2023 ana fara da rabawa marayu hamsin dafaffan abinci haka tace gudanar da hakan ne duk domin ragewa al’umma radadin matsin rayuwa

Advertisement

Rufaidan ta kara da cewar wannan cibiya tana samun kudin wannan ciyarwa ne daga hannu daidaikun Al’umma masu hali

Daga karshe ta bayyana hanyar da za a same ta ga masu son taimakawa za a same ta ta lambar wayar ta kira ko whatapp 07064517451

Aminu sani da zainab zakari cikin wadan da suka samu wannan abinci sun bayyana farin cikin su hadi da godewa Allah da wannan cibiya tare da addu’ar Allah ya kara daga wannan cibiya

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending