Connect with us

News

Ma’aikatan Majalisun Jihohi Za Su Shiga Yakin Aiki

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Ma’aikatan majalisun dokokin jihohi da ke fadin Najeriya sun yi barazanar fara yajin aiki daga ranar Laraba.

Ƙungiya Ma’aikatan Majalisun Dokokin Jihohin Najeriya (PASAN) ta ce za ta tsunduma yajin aikin ne saboda kin ba wa majalisu ’yancin gudanar da kuɗaɗensu da gwamnoni suka yi.

Wasu matasa 76 da ake zargin da shirin  auren jinshi sun fada komar hukumar NSCDC a Gombe.

Ƙungiyar ta sanar cewa mambobinta za su daina aiki su kuma rufe ofisoshinsu, har sai gwamnoni sun gaggauta ba wa majilisun ’yancin gudanar da kuɗaɗensu.

Sakatare-Janar ta PASAN, Agugbue Ugochi Happiness, ta ce wajibi ne gwamnoni su ba wa majalisun jihohi ’yancin cin gashin kansu da gudanar da kuɗaɗensu kamar yadda kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanada.

Advertisement

Ta bayyana cewa za su shiga yajin aikin ne bayan cikar mako guda suka kara a bisa wa’adin mako uku da suka fara ba wa gwamnoni na yin abin da ya dace, wanda ya kare tun ranar 18 ga watan Satumbam 2023.

Sanarwar yajin aikin da ta aike wa Shugaban Kungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) da Hukumar Tsaro ta DSS da kuma Ƙungiyar Shugabannin Majalisun Dokoki, ta bayyana cewa shiga yakin aikin ta zama dole, idan sabon wa’adin ya cika gwamnonin ba su yi abin a zo a gani ba kan lamarin.

Ma’aikatan Majalisun dai sun sha gudanar da zanga-zanga domin ganin majalisu sun samu ’yancin gashin kansu, amma hajar ba ta cim-ma ruwa ba.

“Muna fata za su yi amfani da karin wa’adin su yi abin da ya kamata, su biya mana bukatunmu, ida ba haka ba za mu umarci mambobinmu su fara yajin aikin,” in ji ta.

A wani labarin kuma Wasu matasa 76 da ake zargin da shirin  auren jinshi sun fada komar hukumar NSCDC a Gombe.

Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.

Advertisement

Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.

A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.

Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending