Connect with us

News

Gwanan Oyo ya yi wa ma’aikata ƙarin naira 25,000 a kan albashinsu

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo ya bayyana cewa ma’aikatan jihar da ‘yan fansho za su rika karbar tallafin kudi na naira 25,000 da kuma N15,000 duk wata na tsawon watanni shida har sai an cimma matsaya kan sabon mafi ƙarancin albashi

Advertisement

DA ƊUMI-ƊUMI: Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da nasarar zaɓen ɗan majalisar tarayya na Kura/Madobi/Garin-Malam

Ya kuma jaddada muhimmancin ma’aikata da al’ummar jihar wajen haɗa hannu da gwamnatin jihar domin bunƙasa tattalin arzikin jihar na tsawon lokaci.

Advertisement

Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi ga ma’aikatan a ofishin gwamna, Sakatariya, Agodi a Ibadan.

Ya yi nuni da cewa duk da cewa gwamnatinsa za ta so ta yi aikin da za a riƙa tunawa da su shekaru da dama bayan ya bar mulki, za ta ci gaba da kula da jin daɗin ma’aikatanta.

Advertisement

Za a biya kudaden tallafin ne na tsawon watanni shida masu zuwa, wanda hakan zai sa a samu karin Naira biliyan 2.2 a kan lissafin albashin ma’aikata na wata-wata.

Gwamnan ya cimma yarjejeniya da shugabannin ƙwadago domin aiwatar da wannan shiri.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending