News
Joe Biden Ya Ce An Kusa ƙulla Yarjejeniya tsakanin Isra’ila da Hamas
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Shugaban Amurka Joe Biden ya nuna cewa nan gaba kaɗan za a ƙulla yarjejeniyar da za ta kai ga sakin mutanen da mayaƙan da Hamas ke garkuwa da su a Zirin Gaza.
Rahotonni sun ce Hamas za ta saki wasu daga cikin mutanen a madadin tsagaita wuta na wasu ‘yan kwanaki da Isra’ila za ta yi a hare-haren da take kaiwa a zirin.
Har Yanzu Akwai Gibin Shinkafa Sama Da Tan Milliyan 2 A Najeriya – Bincike
Biden ya yi kalaman ne yayin taron cikaciki na shekara-shekara.
Da wani ɗan jarida ya tambaye shi game da yarjejeniyar da aka ce an kusa ƙullawa, Biden ya bayar da amsa da cewa: “Ina ganin haka”.
A ranar Lahadi, jaridar Washington Post ta ruwaito cewa an kusa ƙulla yarjejeniyar, kuma jakadan Isra’ila a Amurka ya faɗa ranar Lahadi cewa yana da ƙwarin gwiwar za a cimma yarjejeniyar “cikin ‘yan kwanaki masu zuwa”.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
