Connect with us

News

An kama wani mutum mai shekaru 53 bisa laifin yin lalata da kananan yara masu tabin hankali

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

 

Advertisement

Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta kama wani mutum mai shekaru 53 mai suna Usman Ahmadu bisa zarginsa da cin zarafin wata karamar yarinya mai tabin hankali.

Usman Ahmadu, wanda aka ce ya fito daga Maiduguri a jihar Borno, yana zaune ne a matsayin dan gudun hijira, IDP, a unguwar Saminaka da ke wajen Yola, a karamar hukumar Yola ta Arewa.

Advertisement

Najeriya Za Ta Fara Fitar Da Tataccen Mai Kasar Waje A 2024 —NNPCL

Yanzu haka rundunar ‘yan sandan jihar, Usman Ahmadu ya amsa laifin yin lalata da yarinyar mai tabin hankali har sau hudu, tun daga shekarar 2021.

Sanarwar da rundunar ‘yan sandan jihar ta fitar wacce ta bayyana lamarin, ta ce kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Afolabi Babatola, ya bayar da umarnin gudanar da bincike mai zurfi tare da gurfanar da shi gaban kuliya.

Advertisement

Sanarwar wacce jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Suleiman Nguroje, ya saki da safiyar Alhamis, ta ruwaito CP din yana bada tabbacin cewa babu wata maboya ga masu aikata laifuka kamar yanda Jaridar Daily Post ta ruwaito.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending