Connect with us

News

Najeriya Za Ta Fara Fitar Da Tataccen Mai Kasar Waje A 2024 —NNPCL

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

Shugaban Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) Mele Kyari ya ce Najeriya za ta zama kasa mai fitar da tataccen man fetur da dangoginsa zuwa kasashen waje a shekarar 2024 mai kamawa.

Mele Kyari ya kuma ba wa ’yan Najeriya tabbacin cewa cikin watanni uku masu zuwa ba za a samu karancin man fetur ba, kamar yadda ake gani a lokacin bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara.

Advertisement

Mutum 25,000 ne suka ɓace a cikin shekaru 10 a Najeriya – ICRC

“Ina tabbatar wa shugabannin majalisa ba za a fuskanci karancin mai ba.

“Za ku ji ana ta yada labarin layuka a gidajen mai, amma ba gaskiya ba ne,” in ji Mele Kyari.

Advertisement

Ya bayyana hakan ne lokacin da ya ziyarci shugabannin majalisar dattawa.

Ya kara da cewa NNPC zai gyara matatar mai ta garin Fatakwal a wata mai kamawa, sannnan matatar mai ta Warri ta biyo baya a farkon 2024.

Advertisement

Haka zalika, ya yi hasashen NNPCL zai samu ribar da ta kai triliyan biyu a shekarar 2023 da ke dab da karewa.

Kyari ya shaida wa shugabannin majalisar dattawa cewa amincewa da sabuwar dokar man fetur, ta saka man ya wadata kuma a farashi mai sauki a kasar nan.

Advertisement

Da yake jawabi kan matsalar fasa bututu da satar mai, Kyari ya ce jami’an tsaro na musamman da ke yaki da bata-garin, sun taimaka musu wajen kwato gangunan danyen mai na kusan naira miliyan biyu.

Da yake jawabi, shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya gode wa kamfanin man bisa hadin kai da ya bai wa Gwamnatin Tarayya wajen cire tallafin man fetur.

Advertisement

A wani labarin kuma Mutum 25,000 ne suka ɓace a cikin shekaru 10 a Najeriya – ICRC

Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.

Advertisement

Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.

A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.

Advertisement

Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending