News
Mutane mu Suna Cikin Mawuyacin Hali -Kakakin majalisar wakilan Nijeriya
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kakakin Majalisar Wakilai Tajudeen Abbas, ya ce ‘yan Najeriya na cikin mawuyacin hali, ya kuma yi kira da a mai da hankali kan kasafin kudin wajen jin dadin jama’a.
Abbas ya bayyana haka ne a ranar Laraba yayin gabatar da kudirin kasafin kudin 2024 da shugaba Bola Tinubu ya gabatar.
Cire tallafin man fetur da shugaba Tinubu ya yi da kuma hada kan farashin canji ya haifar da hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya.
Kakakin majalisar ya yi gargadin cewa bai kamata a kalli kasafin a matsayin “takardar kudi kawai ba.” Ya kara da cewa kasafin kudin dole ne ya yanke shawara don magance mafi mahimmancin bukatun ‘yan kasarmu da suka dade suna shan wahala.
Shugaban kasa, sanannen abu ne cewa miliyoyin al’ummarmu na rayuwa cikin mawuyacin hali. Don haka ne ma suke sa ran gwamnatin da Tinubu ke jagoranta ta samar da mafita cikin gaggawa da kuma dorewa, inji Abbas.
Da yake magana kan bukatar shugaban kasa na amincewa da kasafin kudin kafin ranar 31 ga watan Disamba, Abbas ya ce kamata ya yi shugaban kasa ya tabbatar da MDAs sun bayyana a gaban kwamitocin domin sauraren korafinsu.
A wani labarin kuma Zaben Kogi:Ba Zanyi Wahalar Zuwa Kotu Ba-Dino Melaye
Najeriya da Angola sun ki amincewa da matakin da kungiyar kasashe masu arzikin fitar da man fetur ta duniya Opec ta bukaci su dauka, na rage yawan man da suke hakowa.
Rahotonni sun bayyana cewa, kawancen Kasashen da Saudiyya ke jagoranta ba su samu cimma matsaya ba da Angola da Najeriya, wadanda suka nuna rashin amincewarsu da rage yawan man da suke hakowa.
Wani wakili a yayin ganawar ya ce ba lallai ba ne a iya cimma matsaya a tsakanin bangarorin biyu kafin taron da kungiyar ta OPEC da za’a yi a gobe 30 ga Nuwambar 2023.
