Connect with us

News

Sojojin Isra’ila sun sake kama Falasdinawa 40 a Yammacin Kogin Jordan

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Rundunar sojin Isra’ila ta tsare aƙalla Falasɗinawa 40 a wani samame da ta kai Yammacin Kogin Jordan da safiyar ranar Alhamis, a cewar Ƙungiyar Fursunoni ta Falasɗinawa.

Trt Afirka ta ruwaito cewa Kungiyar ta Falasɗinu mai zaman kanta ta bayyana cewa kamen na baya-bayan nan ya sa yawan Falasɗinawan da aka tsare tun ranar 7 ga watan Oktoba ya kai 3,365.

Rashin yin adalci a shari’ar zaɓen Kano na iya haddasa tashin hankali – NNPP

Tashin hankali na ƙaruwa a Yammacin Kogin Jordan a yayin da sojojin Isra’ila ke kai hare-hare Zirin Gaza tun bayan harin ba-zatan da Hamas ta kai wa Isra’ila ranar 7 ga watan Oktoba.

A wani labarin kuma Rashin yin adalci a shari’ar zaɓen Kano na iya haddasa tashin hankali – NNPP

Hamas ta yi ikirarin cewa mayakanta ne suka kaddamar da harin Birnin Kudus da safiyar yau, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum uku, kamar yadda kungiyar ta wallafa a shafinta na Telegram.

Advertisement

Cikin sanarwar, Hamas ta ce ”ta kai hari ne saboda mayar da martani kan laifukan da ake aikata wa al’umominta ta hanyar mamaya,” tana mai kafa hujja da ayyukan sojin Isra’ila a Gaza da yadda ta ce ana muzgunawa Falasdinawa a gidajen yarin Isra’ila.

Kamfanin dillancin labarai na AFP, ya ambato sanarwar kungiyar na kira ga mambobinta da su ”ci gaba da fadada juriya”.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending