Connect with us

News

Yan sanda sun kama hadimin gwamnan Kano bisa zargin karkartar da tallafin kayan abinci

Published

on

 

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDI

Advertisement

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta cafke babban mataimaki na musamman ga gwamnan Kano a ofishin sakataren gwamnati Tasiu Al’amin-Roba da kuma wani Abdulkadir Muhammad bisa zargin karkatar da kayan abinci na rage radadin cire tallafin man fetur da gwamnati ta bayar don rabawa al’umma kyauta.

Advertisement

Yadda Hakimai 3 Suka Mutu A Hatsarin Mota A  Jihar Oyo

An kama wadanda ake zargin ne a wani gidan ajiyar kaya da ke Sharada dauke da buhuhunan shinkafa da masara sama da 200.

Advertisement

Da yake tabbatar da cafke mutanen kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, Hussaini Gumel, ya ce sun gano cewa wadanda ake zargin suna sauyawa kayan abincin buhu da nufin siyar dasu ga al’umma, sabanin yadda gwamnati tace a raba kyauta.

Hussaini Gumel ya ce za a gurfanar da mutanen biyu a gaban kotu bayan kammala bincike na gaskiya.
A jiya asabar gwannan Kano Abba Kabir Yusuf ya kai ziyarar gidan a ajiyar kayan, bayan an gano cewa karkatar da kayan abincin don siyarwa, inda gwamnan yayi alkawarin yin bincike tare da hukunta masu hannu a cikin lamarin.

Advertisement

 

Premier

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending