Connect with us

News

Yadda Hakimai 3 Suka Mutu A Hatsarin Mota A  Jihar Oyo

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

 

 

Al’ummar Masarautar Ogbomoso a Jihar Oyo sun kidime da juyayi da rasuwar manyan hakimai uku a hatsarin mota da ya rutsa da su a yankin Arinkinkin da ke Karamar Hukumar Orire.

Hakiman da suka rasu a ranar Juma’a sun hada da Olodogbo na Odogbo da Onibowula na Bowula da kuma Alayetoro na Ayetoro.

An gano wani waje da ake zargin ana sauya buhunhunan kayan tallafin rage raɗaɗin da Gwamnatin Kano ta raba.

Wata majiya mai tushe ta ce, sarakunan da suke cikin mota daya suna kan hanyar zuwa jana’izar dan uwan wani takwaransu wato Oloolo na Oolo Oba Oyebunmi Ajayi ne a lokacin da hadarin ya auku.

Advertisement

Majiyar ta bayyana cewa, motar da suke ciki ce ta yi karo ne da wata babbar mota inda nan take suka rasa rayukansu.

Aminiya ta ruwaito cewa Mutum na hudu da ke cikin motar, wanda ake kyautata zaton direban motar ne ya samu raunuka da yanzu haka likitoci suke kokarin ceton ransa.

 

An kai gawarwarkin Asibitin koyarwa na LAUTECH da ke Ogbomoso.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending