Connect with us

News

Da Ɗumi-Ɗumi: Majalisar dattawa ta tantance alkalai 11 na kotun koli

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

 

Da Ɗumi-Ɗumi: Majalisar dattawa ta tanfanda alkalai 11 na kotun koli

A ranar Alhamis ne majalisar dattawa ta tabbatar da nadin sabbin alkalai 11 na kotun koli.

Tabbatar da nasu ya biyo bayan nazarin rahoton kwamitin majalisar dattijai kan harkokin shari’a da kare hakkin bil’adama da kuma shari’a.

Yadda Ta Kasance A Kotun Koli Akan  Sauraren Karar Zaben Gwamnan Kano 

Majalisar dattijai ta amince da shawarar kwamitin, inda ta tantance wadanda aka nada.

Advertisement

 

Sanatan Borno ta Arewa kuma shugaban kwamitin Sanata Mohammed Monguno ne ya gabatar da rahoton a gaban majalisar dattawa.

 

A ranar Laraba, 20 ga watan Disamba ne shugaban kasa Bola Tinubu ya bukaci majalisar dattawa ta tabbatar da mutane 11 da aka tantance.

 

Hukumar kula da harkokin shari’a ta kasa NJC ta ba da shawarar wadanda aka nada da su cike mukaman da suka taso sakamakon mutuwa da murabus din wasu alkalan kotun koli.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending