Connect with us

News

Yadda Ta Kasance A Kotun Koli Akan  Sauraren Karar Zaben Gwamnan Kano 

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

A yau Alhamis 21, ga watan Disambar 2023, Kotun kolin Nijeriya da ke Abuja ta fara sauraren karar zaben gwamnan Kano da Gwamnan Kano Abba Kabiru Yusuf da Jam’iyyar NNPP da INEC suka shigar gabanta.

Ma su shigar da karar sunan kalubalantar hukuncin kotun sauraren karar zaben gwamnan Kano da Kotun daukaka kara da su suka ayyana dan takarar Jam’iyyar APC, Dr. Nasiru Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Kano.

Ba a Samu Fasa Gidan Yari Ba a Shekarar 2023 – NCoS

A zaman na yau, tunda farko Kotun ta ce, ba ta da lokacin sauraren ƙarar NNPP da Abba da INEC da suka shigar gabanta har guda tara (9), sai dai su zaɓi guda ɗaya a cikin tara.

 

Advertisement

 

 

Daga bisani Kotu ta yi ƙarin haske kan batun satar ƙuri’un zaɓe a Nijeriya, wanda ta ce wajibi ne doka ta yi aiki don magance matsalar ba a iya Kano kaɗai ba a duk faɗin Nijeriya saboda wajibi ne kiyaye doka da oda.

A karshe Kotun ta kammala sauraron ƙarar, ta kuma ce za ta sanar da ranar yanke hukunci kan shari’ar.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending