Connect with us

News

Emefiele, karkashin Mulkin Buhari, ya karkatar da kasafin kudin Najeriya na shekaru 10  -Kazaure

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Tsohon dan majalisar wakilai, Nuhu Gudaji Kazaure, ya yi ikirarin cewa tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele ya karkatar da sama da Naira tiriliyan 89, kwatankwacin shekara 10 na kasafin kudin Najeriya, a lokacin da yake rike da mukamin Gwamnan Babban Bankin CBN daga 2014 zuwa 2022.

Advertisement

Gudaji Kazaure ya bayyana haka ne a lokacin da yake amsa tambayoyi daga shahararriyar tashar Hausa ta DCL da Jaridar INDA RANKA ta  sa ido a kai.

Yanzu-Yanzu: An Saki Emefiele daga gidan Yari bayan ya cika sharadan Beli

A lokacin gwamnatin shugaba Buhari, Gudaji Kazaure ya jagoranci kwamitin binciken kudaden da Emefiele ya karkatar da su. A yanzu ya yi ikirarin tabbatar da gaskiya ne bisa tonon silili daga kwamitin da shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya kafa domin binciken zaman Emefiele a matsayin Gwamnan CBN.

Advertisement

Kwamitin da Tinubu ya nada ya bayyana cewa Emefiele ya gudanar da asusu na kasashen waje sama da 593 inda aka boye kudaden Najeriya.

Gudaji Kazaure ya shaida wa Hausa DCL cewa lokaci ya kure masa, inda ya ce a lokacin gwamnatin Buhari ya yi kokarin ganin tsohon shugaban kasar ya ba su damar ci gaba da binciken domin a rubuta sunan tsohon shugaban da rubutun zinariya. Sai dai kash kokarinsu ya kasance a banza.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending