News
Emefiele Ne Ya Mallaki Rukunin Gidaje 753 Da Hukumar EFCC Ta Ƙwace A Abuja
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Tsohon gwamnan CBN, Emefiele ne ya mallaki rukunin gidaje 753 da Hukumar Yaki da Rashawa da Tattalin Arziki EFCC ta ƙwace a Abuja .
A ranar Litinin hukumar EFCC ta ce ta samu nasarar karɓe gidajen a hannun wani tsohon babban jami’in gwamnati wanda bata fadi sunanshi ba.
Masu Zanga Zanga Sun Yi Wa Majalisar Dokoki Ta Kasa Tsinke Kan Kudirin Gyara Harajin Shugaba Tinubu
Amma wasu takardun shigar da ƙara sun nuna cewa gidan na dakataccen gwamnan babban bankin Nijeriya ne Godwin Emefiele wanda ke fuskantar shari’a.
A cikin takardun kotun da wakilin Jaridar PUNCH ya samu a ranar Talata, EFCC ta bayyana yadda ta gano wannan gida mai girman murabba’in ƙasa 150,500, wanda ke a Plot 109, Cadastral Zone C09, Lokogoma District, Abuja.
Kokarin samun martanin daga lauyoyin Emefiele ya ci tura, domin Matthew Burkaa (SAN) bai amsa kiran waya ko saƙon tes ba a lokacin haɗa wannan rahoto.
Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya kare dalilin hukumar na boye sunan mai gidan. Ya ce dokar da aka yi amfani da ita ta ba da damar kwace dukiya ba tare da ambaton sunan wanda ke da ita ba, musamman idan babu wanda ya nuna mallakar abu.
Ya kara da cewa binciken kan al’amarin bai kammala ba, kuma bayyana sunan waɗanda ake zargi ba zai dace ba a wannan matakin.
