Connect with us

News

Hukumar NDLEA Ta Cafke Masu Safarar Kwaya 198, Sun Lalata Wurin Sayar Da Kwaya 21 A Kano

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Advertisement

Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) a Jihar Kano, ta samu nasara a shirinta na “Operation Hana Maye” na yaki da safarar miyagun kwayoyi a jihar.

Daga ranar 17 ga watan Janairu zuwa 26 ga watan Janairu, 2024 karkashin jagorancin Kwamandan jihar, Abubakar Idris-Ahmad, hukumar ta kama mutane 198 da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi tare da tarwatsa gidajen sarrafa miyagun kwayoyi 21.

Advertisement

FAƊA DA WAN ƘARFI: Dala ta lollotsa wa Naira kumatu, ta gaggaɓe mata haƙoran gaba a kasuwar ƴan canji

Kakakin hukumar, Mista Sadiq Muhammad-Maigatari ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai.

Dakarun hukumar sun kai samamen ne wurare daban-daban, ciki har da wani gidan casu da ya koma wajen hada-hadar miyagun kwayoyi, inda aka kama mutane 61.

Advertisement

Har wa yau, an kama mutane 42 da ake zargi a makabartar Dan Agundi, sannan an tarwatsa gidajen miyagun kwayoyi guda 21 da ke makabartar Sheka da Sheka Obajana.

Daga cikin abubuwan da hukumar ta kwato har da maganin Exol, tabar wiwi, da sauran magunguna masu hatsari.

Advertisement

NDLEA ta sake jaddada aniyarta na kawar da shaye-shayen miyagun kwayoyi da safarar miyagun kwayoyi a jihar.

Hukumar ta ce za ta mayar da hankali wajen kara kaimi don zakulo masu safarar miyagun kwayoyi.

Advertisement

Kwamanda Abubakar Idris-Ahmad, ya bukaci jama’a da su sanya ido tare da kai rahoton masu safarar miyagun kwayoyi a jihar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending