News
Yusif Maitama: Matsalar Da Daliban library and information science tazo Karshe —Sabon Shugaban Dalibai
DAGA B.IMAM
A ranar Alhamis din data gabata ne aka rantsar da sabbibin Shugabancin daluban Jami’ar Yusif Maitama Sule dake Jihar Kano na bangaran sanin ilimin dakin karatu da kimiyyar sanin bayanai wato Library And Information Science.
Rahotanni na nuni da cewar rantsuwar ta gudana ne a cikin jam’ar a ofishin shugaban tsangayar fannin koyo da koyarwa na ruko dauda muhammad yakasai
Zababban shugaban dalinan Abdullahi Haruna Abdullah ya godewa Allah bisa wannan matsayi daya samu kuma yana mai bayyanawa dalibai da izinin Allah zasu ga canji da jagoranci na gari a cikin Makaranatar.
A nasa bangaran Abubakar Rabi’u Abubakar Captain dake a matsayin tsohon dan takarar shugabancin kungiyar dalibai a jami’ar yace a shirye yake da ya bada shawarwari ga zababban shugaban daliban Jami’ar Mujahid Bamalli
Dr.Dauda Muhammad Yakasai da ya jagoranci rantsuwar yaja hankalin sabbin shugabannin dasu kasance masu tsoron Allah da rikon Amana tare da yin kira ga dalibai dasu baiwa sabbin jagororin dalibai hadin kai tare da girmamawa.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
