Connect with us

News

Dalilin Da Ya Sa Ban Yi Musabaha Da Gwamna Abba Yusuf  Ba – Ahmed Musa

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Kaftin din kungiyar kwallon kafa ta Nijeriya (Super Eagles), Ahmed Musa, ya magantu kan cece-kucen da ake ta yadawa a shafukan sada zumunta dangane da yadda ya yi mu’amala da Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano a ziyarar da ya kai gidan gwamnati a watan da ya gabata.

Leadership ta ruwaito cewa a wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta ya nuna Musa ya durkusa wa gwamnan ba tare da yin musabaha ba, lamarin da ya haifar da cece-kuce a tsakanin masu amfani da kafafen sada zumunta.

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Gamboro Da Ke Maiduguri A Jihar Barno

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata a shafinsa na X (Twitter), Musa ya fayyace cewa, matakin nasa ya samo asali ne daga al’adun mutuntawa na gari, maimakon yadda wasu ke ganin cewa, rashin mutuntawa ga Gwamna Yusuf.

Ya jaddada cewa, a al’adun Arewacin Nijeriya, ayyuka irin su durkusawa suna nuna girmamawa ga masu daraja.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending