Connect with us

News

Kotun Da’ar ma’aikata ta dakatar da Muhyi Magaji daga shugabancin hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

A wani mataki da ka iya girgiza yunkurin jihar Kano na yaki da cin hanci da rashawa, Kotun da’ar ma’aikata ta dakatar Muhuyi Magaji daga shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne aka gurfanar da Magaji a gaban kuliya bisa manyan zarge-zarge, da suka hada da saba ka’idojin da’a ga jami’an gwamnati, da yin rikici da juna, cin zarafin ofishinsa, da bayar da bayanan karya kan bayyana kadarorinsa.

Dalilin Da Ya Sa Ban Yi Musabaha Da Gwamna Abba Yusuf  Ba – Ahmed Musa

Ana kuma zarginsa da cin hanci da karbar kyaututtuka.

Kotun ta goyi bayan wanda ya shigar da karar, inda ta umurci Magaji da ya ajiye mukaminsa na Shugaban Hukumar.

Ba zai iya cika aikinsa a Hukumar Korafe-korafe da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ba har sai an saurari tuhume-tuhumen da ake yi masa, sannan a yanke hukunci.

Advertisement

Bugu da kari, kotun ta umurci gwamnan jihar Kano da sakataren gwamnatin jihar da su nada shugaban riko na hukumar domin tabbatar da ci gaba da gudanar da ayyukan hukumar a wannan lokaci.

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending