News
Da Dumi Dumi: Kotu Ta Tabbatar Da Dakatarwar Da Aka Yi Wa Ganduje Daga Shugaban Jam’iyyar APC
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Babbar Kotun Jihar Kano ta tabbatar da dakatarwar da aka yi wa Shugaban Jam’iyyar APC na Kasa, Dokta Abdullahi Umar Ganduje, daga jam’iyyar.
An dai dakatar da tsohon gwamnan Kano, Ganduje, daga Jam’iyyar APC ne a mazabarsa, kan zargin rashawa.
Cutar Zazzabi Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutune 45 A Kauyen Jihar Kano
A ranar Litinin ne dai shugabancin jam’iyyar na mazabar Ganduje suka sanar da dakatar da shi.
Amma daga bisani wani sashi na shugabancin jam’iyyar an kuma na jiha ya sanar da korar wadanda suka sanar da dakatar da Gandujen.
Kotun dai ta dage sauraron karar zuwa ranar 30 ga watan Afrilu, 2024.
Wannan dai na zuwa ne a ranar da hukumar yaki da rashawa ta jihar Kano ke sa ran gufanar da Ganduje da gaban kuliya kan zargin almundahana a zamanin mulkinsa a jihar.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
