News
Cutar Zazzabi Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutune 45 A Kauyen Jihar Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kimanin mutane 45 ne aka ruwaito sun rasa rayukansu sakamakon barkewar wata cuta mai ban mamaki a kauyen Gundutse da ke karamar hukumar Kura a jihar Kano.
Bayanai sun ce mata da kananan yara da tsofaffi ne cutar ta fi yi wa illa. Daga cikin alamun cutar akwai zazzabi mai zafi, amai da gudawa.
Idan Isra’ila ta kaiwa Iran hari babu ruwanmu a ciki – Amurka
Daily Trust ta ruwaito cewa Mazauna yankin sun bayyana damuwarsu game da karuwar mace-macen ba zato ba tsammani a cikin makonni biyun da suka gabata.
Sai dai lamarin ya zama mai firgitarwa yayin da al’ummar kasar suka fara binne mutane biyar a kullum, lamarin da ke nuni da cewa an samu matsalar rashin lafiya.
Abu Sani, wani mazaunin garin da ya rasa ‘ya’ya biyu, ya ce da farko ‘yan uwansa sun yi tunanin cutar zazzabin cizon sauro ce ke damun dansa dan shekara biyu, wanda ya mutu cikin bakin ciki duk da taimakon likitoci.
Jami’an lafiya a asibitin na Gundutse sun shaida wa wakilin jaridar Daily trust a ziyarar da suka kai cewa kawo yanzu an samu rahoton mutuwar mutane 20.
Daya daga cikin ma’aikatan lafiya a asibitin, wanda ya so a sakaya sunansa, ya ce tuni sun kai rahoton faruwar lamarin ga ma’aikatar lafiya ta jihar
Da aka tuntubi Jami’an yada labarai na Ma’aikatar lafiya na jihar Kano, Ibrahim Abdullahi, ya ce zazzabin materia ne ya kara da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano ainihin musabbabin mutuwar.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
