Connect with us

News

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Shirinta Na Sake Duba Farashin Lasisin Hakar Ma’adanai

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Gwamnatin tarayya ta bakin ma’aikatar bunkasa ma’adanai ta kasa, ta bayyana shirinta na sake duba farashin lasisin hakar ma’adanai da sauran kudaden da masu aikin hakar ma’adanai ke biya a kasar nan.

Advertisement

SOLACEBASE ta ruwaito cewa Hakan a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mataimaki na musamman ga karamin ministan ma’adanai na kasa Segun Tomori.

Gwamnatin Tarraya ta hana amfani da sirinji da allura na kasashen waje a manyan asibitoci

Da yake jawabi yayin wani taron tuntuba na masu ruwa da tsaki a jiya Alhamis a Abuja, Ministan ya bayyana cewa shirin zai inganta kudurin gwamnati na sake farfado da bangaren ma’adinai yadda ya kamata.

Advertisement

Ya jaddada cewa sake duba farashin ya zama wajibi idan har gwamnati za ta dauki nauyin da ya rataya a wuyanta na samar da yanayi mai kyau ga ayyukan hakar ma’adinai tare da kara samun kudaden shiga.

Ministan ya nemi goyon bayan masu ruwa da tsaki kan karin kudin lasisin hakar ma’adinai da sauran kudaden da suke da kudurin yin karin su a nan gaba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending