Connect with us

News

Hukumar dake kula da gidajen gyaran hali  ta dakile yunkurin shigar da miyagun ƙwayoyi gidajen yari

Published

on

DAGA MUHAMMAD BASHIR MUSA 

Hukumar kula da gidajen gyaran hali ta Najeriya ta yi nasarar dakile yunkurin shigar da miyagun kwayoyi zuwa gidajen yari.

Advertisement

Mai Magana da yawun hukumar reshen birnin tarayya Abuja, DSC Adamu Duza ne ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fita ranar Alhamis a Abuja.

An Kashe Matashi Saboda Bacewar Hula A Bauchi

Ya ce “Bayan sanya ido da tsaurara bincike, mun damke dillalan muyagun kwayoyi a gidan gyaran hali da ke Kuje. Jami’an dake kula da tsaron Kuje Da misalin karfe uku na ranar Laraba, sun kama wani mutum mai suna Fidelis Emmanuel da wani abu da ake zargin tabar wiwi ce”

Advertisement

 

 

Advertisement

“A yayin da ake gudanar da bincike, an gano cewa wanda ake zargin ya zo da abinci a cikin kwano domin ziyaratar abokinsa da ke tsare. Ana cikin duba shi ne aka gano muggan kwayoyin da ya boye a kasan kwanon abinincin,kuma yanzu haka wanda ake zargin yana tsare”

 

Advertisement

Duza ya ce, Kwanturolan hukumar a Auja, Mista John Francis ya bayar da umarnin mika wanda ake zargin ga hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA) domin daukar matakin doka a kanshi.

 

Advertisement

 

Ya ce, kwanturolan ya kuma kara tsaurara matakan tsaro da zasu sanya ido a cibiyoyin da ke cikin birnin tarayya Abuja, domin gano wadanda suke fakewa da ziyara suna safarar miyagun kwayoyi zuwa cibiyoyin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending