Connect with us

News

Jaridun Najeriya: Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani A Safiyar Ranar Asabar

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

1 — Aikin gyare-gyaren titin Eastern Bypass a cikin birnin Kano ya yi sanadiyar mutuwar mutum shida cikin makonni uku zuwa hudu.

Advertisement

 

2 — Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya NLC ta ce gwamnonin jihohin ƙasar za su iya biyan fiye da naira 60,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi, idan suka rage cin hanci da rashawa da kuɗin da suka kashewa wajen gudanar da mulki a jihohinsu.

Advertisement

Yadda wani mai gidan haya ya sheka lahira yayin musu da ɗan haya

3— Wani gungun ‘yan ta’adda da aka fi zaton cewa mayakan kungiyar Boko Haram ne sun kashe a kalla mutane 20 a wasu hare-hare da suka kai a karamar hukumar Shiroro da Bassa da ke jihar Neja.

 

Advertisement

4— Tsarin zamanantar da kasuwanci na hukumar kwastom TMP zai magance matsantawa ‘yan kasuwa ta hanyar bin diddigin kayayyakinsu tun daga farkon siyo kayan zuwa kaiwa gare su.

 

Advertisement

5—Ofishin Jakadancin Saudiyya da ke Abuja, ya shirya bikin bankwana ga mahajjatan Nijeriya da za su halarci aikin Hajjin 2024.

Ambasada Faisal Ibrahim al-Ghamidy ne, ya jagoranci bikin wanda manyan jami’ai daban-daban, manyan baki, da kuma wasu mahajjatan da suka halarci taron.

Advertisement

 

6— Kungiyar Daraktocin Bankunan Najeriya ta bayyana kwarin gwiwar cewa matakin da babban bankin Najeriya ya dauka na soke lasisin bankin Heritage ya kasance mafi alheri ga bangaren bankuna.

Advertisement

Shugaban kungiyar Mustapha Chike-Obi ne ya bayyana hakan a wata hira da jaridar PUNCH.

 

Advertisement

7— Domin ragewa jama’a radadin kuncin rayuwa lokacin bikin Sallar Layya, Gwamnan Katsina Dikko Umar Radda ya amince a rabawa ma’aikatan jiharsa naira dubu 45 kowanne mutum guda. Sanarwar gwamnatin tace naira dubu 30 rance ne da za’a cire a cikin albashin watanni 3, yayin da kuma dubu 15 garabasa ce daga gwamnati.

8— Kotun soji a Kinshasa dake Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo ta fara shari’ar wasu mutane 53 da ake zargi da yunkurin juyin mulki a kasar, cikin su harda wasu Amurkawa. Wannan ya biyo bayan wani hari da mutanen dauke da makamai suka kai ranar 19 ga watan Mayu.

Advertisement

 

9—Fitacciyar jarumar fina-finan Kannywood Hadiza Gabon ta bukaci mata da su daina shiga masana’antar Kannywood, inda ta bayyana cewa illar shiga masana’antar da mata ke fuskanta ya fi alfanu dake cikin masana’antar.

Advertisement

 

10— Sabon dan wasan Real Madrid, Kylian Mbappe, ya saka hannu kan kwantiragin komawa Real Madrid daga Paris St-Germain, idan yarjejeniyarsa ta kare ranar 30 ga watan Yuni.

Advertisement

Tun cikin watan Fabrairu dan wasan na tawagar Faransa ya amince baka da baka da cewar zai koma Sifaniya, sannan cikin watan Mayu aka sanar da zai bar PSG a karshen kakar nan.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending