Connect with us

News

Rikicin Masarautar Kano: Rundunar ‘Yan Sandan Kano ta gargaɗi mutane kan ƙauracewa tashin-tashina

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Yayin da babbar kotun tarayya da ke Kano ke yin hukunci kan wasu al’amura da suka shafi Masarautar Jihar a yau, rundunar ‘Yan sandan Jihar ta yi kira ga al’umma da su gujewa dukkan abun da zai janyo rikici ko hayaniya a dukkan sassan Jihar.

Advertisement

Kakakin Rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya faɗi haka cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis inda ya ce haƙƙin hukumarsu ne su kula da rayuka da dokiyoyin al’ummar Jihar, dan haka kar su amincewa duk wani yunƙuri na tada-zaune-tsaye a lokacin gudanar da shari’ar ko bayan haka.

Kotu Ta Dage Lokacin Da Za Ta Yanke Hukunci Kan Rikicin Masarautar Kano Zuwa Nan Da ‘Yan Sa’o’i Kaɗan 

A ƙoƙarinta na hana ɓarna ta dukkan hanyoyin da suka dace, rundunar ta gargaɗi mutane da su kiyaye abubuwa kamar haka:

Advertisement

 

Na farko, Rundunar tare da sauran hukumomin tsaro da gwamnatin Jihar, sun dakatar da zanga-zanga tare da nau’in taro mai alaƙa da hakan, dan haka jama’a su kiyaye. Sannan duk wanda aka kama da hanu cikin aikata hakan, to doka za ta yi aiki a kansa.

Advertisement

 

Na biyu, za’a sanya jami’ai a wurare da dama, saboda haka ake so al’umma ta basu haɗin kai ta yadda za su ke sanar da su duk wani bayani mai muhimmancin da aka san zai taimaka wajen tabbatar da tsaro.

Advertisement

 

Na uku, hukumar ta buƙaci tawagar ƴan banga da mafarauta da makamantansu da su ƙauracewa shiga cikin harkar tsaron a kowane yanki na Jihar.

Advertisement

Daga ƙarshe, rundunar ta ce, za’a iya neman su ta kafofin Facebook, Twitter, Instagram, da TikTok a adireshin ‘Kano State Police Command’ da kuma ‘NPF Rescue Me’ a manhajar ‘Play Store’, ko kuma ta lambobi kamar haka; 08032419754, 08123821575 09029292926

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending