Connect with us

News

Mutum Biyu Sun Kamu Da Cutar Kwalara A Katsina, 118 Kuma Na Karɓar Kulawa

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Hukumar kula da kiwon lafiya a matakin farko ta Jihar Katsina, ta ce an tabbatar da cutar kwalara ta kama mutum biyu a ƙaramar hukumar Kusada, da ke jihar tare da wasu 118 da a ke binciken lafiyarsu.

Advertisement

A cewar hukumar, tuni an ɗauki matakan fara amfani da tsarin kula da al’amuran da ke faruwa domin hana yaɗuwar cutar da sauran cutukan da za a iya rigakafinsu a jihar.

An gano Bullar Cutar kwalara a Jahar Katsina bayan ta yi ajalin mutum biyu

Daraktan kula da cutuka na hukumar, Dakta Kabir Sulaiman, a wani taron manema labarai a cibiyar bayar da agajin gaggawa ta hukumar, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta ɗauki matakan shawo kan cutar.

Advertisement

Dakta Sulaiman ya ce jihar ta shirya tsaf don daidaita lamarin ɓullar cutar tare da samar da tsarin sa-ido don gano masu kamuwa da cutar.

Hukumar yaki da cutar kwalara ta duniya, ta bayyana Jihar Katsina a matsayin yankin da ke fama da cutar kwalara, inda ake ganin ƙananan hukumomi 10 suna cikin hatsarin kamuwa da ita.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending