News
Shirin Arewa Na Tsige Shugaba Tinubu Daga Mulki Zai Iya Wargaza Najeriya – Shehu Sani
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Tsohon Sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani, ya yi gargadi ga shugabannin Arewa da su yi watsi da shirinsu na tsige shugaban kasa Bola Tinubu daga kujerarsa a zaben shugaban kasa na 2027.
Sani ya yi wannan gargadin ne a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Arise wanda DAILY POST ta lura, inda ya ce irin wannan mataki na iya lalata hadin kan Najeriya.
Wata Babbar Motar Tirela Ta Kashe Masu Sallar Juma’a 14, Tare Da Raunata Da Dama A Kano.
Mai sharhin al’umma ya bukaci shugabannin Arewa da su sanya ido a kan manufofi da shirye-shiryen gwamnatin Tinubu da za su amfani yankin Arewacin Najeriya, maimakon kokarin samun karin karfin siyasa.
Idan za’a tuna cewa Arewacin Najeriya na fama da matsalar rashin tsaro da talauci da dai sauransu.
“Akwai shaidun hada karfi da karfe, da sake haduwa da sojoji- ‘yan siyasa daga Arewa- suna kokarin yin amfani da tsohon shugaban kasa Buhari wajen taron korar gwamnatin Asiwaju Ahmed Bola Tinubu kuma suna fatan sake farfado da damar siyasarsa a cikin gidan talakawa da kuma bayyana gwamnatin a matsayin wacce ta yi wa Arewa zagon kasa kuma wadda ba ta cika alkawuran yakin neman zaben da ta yi wa yankin ba kasancewar tana da mafi yawan kuri’u daga can. Kuma dole ne in yi gargadin cewa yunƙurin yin hakan na iya haifar da babbar matsala ga ƙasarmu.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
