News
Kotun Ɗaukaka Kara Ta Mayar Da Yan Majalisar Dokokin Jihar Rivers Yan Ɓangaren Nyeson Wike
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Kotun ɗaukaka ƙara a Abuja ta soke dakatarwar da wata babbar kotun jihar Rivers ta yi wa ‘yan majalisar dokokin jihar na bangaren Ministan birnin taraiya Abuja Nyeson Wike a watan Mayun wannan shekara ta 2024.
Jaridar premium Times ta ruwaito cewa A wancan lokaci dai kotun ta jihar Rivers ɗin ta haramtawa wadannan yan majalisar su 24 shiga zauren Majalisar su gudanar da duk wani zama da sunan majalisar dokokin jihar ta Rivers, sannan ta hana Martin Amaewhule baiyana kan shi a matsayin kakakin majalisar.
Kotun ta yi haka ne saboda ƙara da aka shigar ake bukatar ta aiyana ƙwace kujeru su na majalisar saboda sauya sheƙa da suka yi daga PDP zuwa APC, saidai wannan kotun ta ɗaukaka ƙara saɓanin wancan hukunci ta yi inda ta ce Martin Amaewhule da yan majalisar 24 na ɓangaren Wike su ne halastattun yan majalisar.
-
News5 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
