News
Jami’yyar Adawa Ta Labour Ta Karɓe Mulki Bayan Shekaru 14 A Birtaniya
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Jami’yyar adawa ta Labour ta kawo karshen shekara 14 na mulkin Jam’iyyar Conservative a kasar Birtaniya.
Kazalika Labour ta kwace kujerar tsohuwar fira ministar Birtaniya Liz Truss da ke wakiltar mazabar Norfolk ta Kudu maso Yamma a Majalisar Dokokin kasar.
JAMB Ta Bankaɗo Dalibai 3,000 Na Bogi Da Suka Kammala Karatu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Jam’iyyar Labour ta kafa tarihin doke Conservative ne bayan zaben ranar 5 ga watan Yuli inda ta samu rinjayen kujeru a majalisar dokokin kasar.
A yayin da zaben ke ci gaba da kirga kuri’u, Fira Minista Rishi Sunak, ya amsa shan kayi.
Ya sanar da cewa, “na dauki laifin wannan faduwa da muka yi.”
Da wannan shan kaye, Rishi Sunak zai sauka daga kujerar Fira Ministan, wadda Shugaban Jam’iyyar Labour, Keir Starmer, zai dare domin kafa sabuwar gwamnati.
Da yake jawabi, Starmer ya ce, “yau mun bude wani sabon babi a Birtaniya.”
Ya ci gaba da cewa, “nasarar zabe ba daga sama take fadowa ba, sai da yaki da gwagwarmaya.
“Shi ya sa a wannan karo Jam’iyyar Labour ta kai ga narasa.”
-
News3 days ago
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
-
News2 days ago
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
-
News3 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
