Connect with us

News

Ranar Lahadi Ce 1 Ga Watan Muharram — Sarkin Musulmi

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

Sarkin Musulmi, Alhaji Abubakar Sa’ad III, ya bayyana cewa gobe Lahadi ce za ta zama 1 ga watan Muharram na sabuwar shekarar Musulunci ta Hijira 1446.

Advertisement

Shugaban kwamitin da ke bai wa Sarkin Musulmi shawara kan harkokin addini, Farfesa Sambo Wali Junaid ne bayyana hakan a ranar Juma’a.

Shugaba Tinubu ya yi kuskure wajen aiwatar da cire tallafin fetur —Tsohon Mataimakin Gwamnan  CBN 

Farfesa Junaid ya ce kwamitin haɗin gwiwa da kwamitin ganin wata na Nijeriya sun tabbatar ba a samu ganin watan Muharram na shekarar 1446 a ranar Juma’ar ba, abin da ke nuna ranar Asabar za ta zama 30 ga watan Zhul Hijja na shekarar 1445.

Advertisement

“Sakamakon haka, Asabar [6 ga watan Yuni] ta zama 30 ga watan Zulhijja 1445…Lahadi kuma [7 ga Yuni] ta zama 1 ga watan Muharram 1446,” a cewar shugaban kwamitin ganin wata na fadar sarkin Musulmi, Farfesa Sambo Wali cikin wata sanarwa.

“Sarkin Musulmi na taya Musulmin Nijeriya murna [sabuwar shekara] da kuma roƙa musu alheri da taimakon Allah,” in ji sanarwar.

Advertisement

Sarkin Musulmin ya roƙi jama’a su ci gaba da addu’ar zaman lafiya da samun ci gaba a ƙasa baki ɗaya.

A tsarin Musulunci, kowane wata kwana 29 ne amma idan aka kasa ganin jaririn sabon wata akan cika watan zuwa kwana 30.

Advertisement

 

Aminiya

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending