Connect with us

News

Da Dumi-Dumi :Majalisar Wakilan Nijeriya Ta Bukaci Ayi Gaggawar Dakatar Da Yarjejeniyar SAMOA

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Majalisar Wakilan Nijeriya ta bukaci gwamnatin Tinubu ta yi gaggawar dakatar da yarjejeniyar SAMOA da ta haifar da cece-kuce da zargin taba martabar addini da al’adun mutanen Nijeriya.

Majalisar ta kuma yanke shawarar bincikar yarjejeniyar da gwamnatin tarayya ta rattabawa hannu a ranar 28 ga watan Yuni.

Babu wata matsala tattare da yarjejeniyar SAMOA — Kungiyar lauyoyin Nijeriya

An zartar da kudurin ne biyo bayan amincewa da kudirin gaggawa na Ali Sani Madaki,  sashin  marasa rinjaye, da wasu ‘yan majalisa 87 suka dauki nauyi.

Kwanan nan yarjejeniyar ta haifar da cece-kuce saboda rahotannin cewa an shigar da tanade-tanade da suka shafi ‘yan madigo, ‘yan luwadi, bisexual, da transgender (LGBT) a cikin yarjejeniyar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending