Connect with us

News

Toshon Akanta Janar Ya Nemi Ƙarin Lokaci Don Maida Kuɗin Da Ya Sace

Published

on

Ofishin hukumar EFCC da ke Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya. © EFCC

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN.

Tsohon muƙaddashin Akanta Janar na Najeriya, Anamekwe Nwabuoku, ya roƙi mai shari’a James Omotoso na babbar kotun ƙasar da ke Abuja kan ya ƙara masa lokaci domin ya kammala mai da kuɗaɗen al’umma da ake zargin su yi rub da ciki akai, shi da Felix Nweke.

Advertisement

Tun da farko hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa ta gurfanar da su a gaban kuliya, bisa wasu zarge-zarge da su ka shafi almundahanar kuɗaɗe.

El-Rufai : Ku Shirya Kare Kanku Ga Hukumomin Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa – Majalisar Dokokin Jihar Kaduna

Nwabuoku da Felix Nweke dai, suna fuskantar tuhume-tuhume 11 game da almundahanar kuɗaɗen da suka Naira Biliyan da miliyan ɗari 6.

Advertisement

Ana kyautata zaton Nwabuoku ya aikata laifin ne yayin da ya rike muƙamin Daraktan kuɗi a ma’aikatar tsaron ƙasar tsakanin shekarar 2019 zuwa 2021.

Yayin da shi kuma wanda ake tuhuma na biyu Felix Nweke, ya taimaka wajen kitsa kitimurmurar, kwashe kuɗaɗen, tare da yin kasha-mu-raba.

Advertisement

A ranar 20 ga watan Mayun shekarar 2022 ne, tsohon shugaban ƙasar Muhammadu Buhari, ya naɗa Nwabouku a matsayin muƙaddashin babban akanta na ƙasar, ƴan kwanaki bayan da aka dakatar da tsohon babban akanta Ahmad Idris, bisa zargin yin hafzi da Naira Biliyan 80.

 

Advertisement

 

Fri

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending