Connect with us

News

Mahaifiyar Dauda Kahutu Rarara Ta Kubuta Daga Hannun ‘Yan Bindiga 

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Mahaifiyar fitaccen mawakin siyasar nan na Arewacin Nijeriya, Dauda Kahutu Rarara ta kubuta daga hannun ‘yan bindigar da suka sace ta.

Idan ba a manta ba an sace mahaifiyar mawakin, Hauwa’u Adamu a ranar 28 ga watan Yuni, 2024 a kauyen Kahutu da ke karamar hukumar Danja a Jihar Katsina.

Da Dumi-Dumi: Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf Ya Naɗa Sababbin Sarakuna A Gaya Da Rano Da Ƙaraye

Sai dai bayan sace tsohuwar mai shekaru 75 a duniya, jami’an ‘yansanda a jihar suka baza koma, inda suka cafke mutum biyu da suke zargi da hannu a sace ta.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, ASP Abubakar Aliyu, ya ce an sace mahaifiyar mawakin da misalin karfe 1:30 na dare.

Ya zuwa yanzu dai an tabbatar da kubutar mahaifiyar mawakin, amma babu cikakken bayani ko an biya kudin fansa kafin sakinta.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending