News
Mahaifiyar Dauda Kahutu Rarara Ta Kubuta Daga Hannun ‘Yan Bindiga
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Mahaifiyar fitaccen mawakin siyasar nan na Arewacin Nijeriya, Dauda Kahutu Rarara ta kubuta daga hannun ‘yan bindigar da suka sace ta.
Idan ba a manta ba an sace mahaifiyar mawakin, Hauwa’u Adamu a ranar 28 ga watan Yuni, 2024 a kauyen Kahutu da ke karamar hukumar Danja a Jihar Katsina.
Da Dumi-Dumi: Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf Ya Naɗa Sababbin Sarakuna A Gaya Da Rano Da Ƙaraye
Sai dai bayan sace tsohuwar mai shekaru 75 a duniya, jami’an ‘yansanda a jihar suka baza koma, inda suka cafke mutum biyu da suke zargi da hannu a sace ta.
Kakakin rundunar ‘yansandan jihar, ASP Abubakar Aliyu, ya ce an sace mahaifiyar mawakin da misalin karfe 1:30 na dare.
Ya zuwa yanzu dai an tabbatar da kubutar mahaifiyar mawakin, amma babu cikakken bayani ko an biya kudin fansa kafin sakinta.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
