Connect with us

Politics

Mataimakin Gwamnan Jihar Edo, Philip Shaibu Da Aka Dawo Da Shi Kwanan Nan Ya Koma Jam’iyyar APC A Hukumance.

Published

on

Spread the love

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Mataimakin gwamnan jihar Edo, Philips Shaibu a ranar Asabar ya fice daga jam’iyy PDP zuwa APC.

Shaibu tare da wasu mambobin gamayyar jam’iyyar PDP ne ya sanar da sauya shekarsa a Benin a taron kaddamar da majalisar yakin neman zaben jam’iyyar na kasa a zaben gwamnan jihar da za a yi a ranar 21 ga watan Satumba.

Advertisement

Dubun Dubatar Al’uma Ne Suka Fito Domin Raka Sarki  Aminu Ado  Rufe Taron Khatamar Al’qur’ani A Kano 

Dakta Abdullahi Umar Ganduje, shugaban jam’iyyar APC na kasa da sauran mambobin kwamitin ayyuka na kasa (NWC) da suka tarbi mataimakin gwamnan, sun ce sun zo ne domin karawa jam’iyyar daraja.

A cewarsa, tabbas jam’iyyar adawa za ta karbe jihar bayan zaben gwamna.

Shi ma Shaibu ya samu karbuwa sosai daga Sanata Adams Oshiomhole, wanda mataimakin gwamnan ya kira mahaifinsa.

Advertisement

NAN, ta rawaito cewa an samu matsala ga Shaibu a jam’iyyar PDP lokacin da ya nuna sha’awar tsayawa takarar gwamna.

Burin dai ya sa mataimakin gwamnan ya kalubalanci shugaban sa, Gwamna Godwin Obaseki, wanda a karshe ya kai ga tsige mataimakin a ranar 18 ga watan Maris da majalisar dokokin jihar ta yi.

Sai dai wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi watsi da tsige shi a ranar Larabar da ta gabata, inda ta ce laifin da aka tsige shi bai kai na rashin da’a ba.

Advertisement
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *