News
Tunibu ya naɗa Masari a matsayin shugaban hukumar gudanarwa ta ilimin manyan makarantu – Tetfund
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya amince da naɗa Tsohon Gwamnan Jihar Katsina Malam Aminu Bello Masari a matsayin shugaban gudanarwar hukumar kula da ilimin manyan makarantu ta Tetfund.
Wannan na ƙunshe ne ta cikin wata sanarwa da Mai baiwa Shugaban Ƙasa shawara kan kafafen watsa labarai Chief Ajuri Ngelale ya fitar a ranar Talata.
Sauran mambobin Hukumar gudanarwar akwai Sanata Sani Danladi da Mr. Sunday Adepoju da Mr. Nuruddeen Adeyemi.
Kafa wannan sabbin mambobin Hukumar gudanarwa ana saran zai zama wata hanya da zata kawo cigaba da inganta ilimin manyan makarantun ƙasar daya
Advertisements
