Connect with us

News

Daliban Da Suka Kai Jami’ar Al-Qalam Kara, Sun Yi Nasara Kotu

Published

on

Al-Qalam

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Babbar kotun jihar Katsina ta umurci hukumar gudanarwar jami’ar Al-Qalam da ke Katsina da ta ba tsoffin dalibanta biyu Hawwa’u Sani Barda da Rabi’atu Sani Barda sakamakon kammala digirinsu.

Advertisement

Kazalika, kotun ta umurci hukumar gudanarwar jami’ar da ta lamunce wa wadannan dalibai zuwa shirin yi wa kasa hidima biyo bayan kammala karatun digiri da suka yi a jami’ar.

Akalla Mutane Biyar Ne Suka Mutu Sakamakon Kifewar Wani Kwale-kwale A Jigawa

Bugu da kari, kotun ta umurci hukumar gudanarwar jami’ar da ta biya tsoffin daliban tarar kudi Naira milyan daya saboda bata musu lokaci da ta yi wajen sanya su cikin shirin yi wa kasa hidima na NYSC bisa zargin da jami’ar ta yi musu cewa ba su biya kudin rajista ba na zangunan karatu hudu.

Advertisement

Daliban, ‘yan’uwan juna, sun maka jami’ar Al-Qalam Katsina kotu, inda suke kararta kan hana su sakamakon kammala digiri da kuma kin sanya su cikin shirin yi wa kasa hidima na NYSC.

Jami’ar Al-Qalam Katsina, jami’ar mai zaman kanta ya zargi daliban, Hawwa’u Sani Barda da Rabi’atu Sani Barda da Hafsat Sani Barda da cewa ba su biya kudin rajista na jami’ar ba na tsawon zangunan karatu hudu, zargin da daliban suka musanta.

Advertisement

Mai ƙwacen waya’ da mota ta buge a jihar Kano ya rasu

Da yake yanke hukunci, Mai Shari’a Abbas Bawale, ya ce bayan sauraren hujjojin da lauya ya gabatar, kotu ta gano cewa Hafsat Sani Barda da Rabi’atu Sani Barda sun biya kudin rajistar karatunsu na tsawon zangunan karatu hudu.

Advertisement

Alkalin ya ce hukumar gudanarwar jami’ar Al-Qalam Katsina ta gaza gamsar da kotu cewa wadannan dalibai ba su biya kudin rajista ba.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending