News
Zaben Kananan Hukumomi A Kano: Babu Gudu Ba Jada Baya Akan Miliyan 10 Da Miliyan 5 A Matsayin Kudin Tsayawa Takarar Chairman Da Kansila —KANSIEC
Hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSIEC, ta ce ba gudu ba ja da baya kan kudaden tsayawa takarar shugabancin kananan hukumomi da kansiloli a jihar.
Hukumar dai ta sanya Naira miliyan 10 ga duk wanda ke son tsayawa takarar shugabancin karamar hukuma da kuma Naira miliyan 5 ga kansila.
Rahotanni na nuni da cewa sanya kudaden dai ya janyo suka daga jam’iyyun adawa wadan suka bayyana matakin a matsayin yunkurin hana su tsayawa takara.
Sai dai shugaban hukumar zaben Parfesa Sani Lawan Malumfashi, ya yi watsi da karafen-korafen, ya na mai cewa ba gudu ba ja da baya.
Akan sanya Naira miliyan 10 ga duk wanda ke son tsayawa takarar shugabancin karamar hukuma da kuma Naira miliyan 5 ga kansila.
NAN
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
