News
Zargin ɓata Suna :Kotu ta tura ɗan jarida gidan yari saboda ɓata sunan Gwamnatin Abba
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kotu ta tura ɗan jarida gidan yari saboda ɓata sunan gwamnan Kano
An tasa keyar wani dan jarida Muktar Dahiru, a gidan yari saboda yada wani labari na zargin Gwamna Abba Yusuf
‘Yan sanda sun kama Muktar Dahiru, ma’aikaci a gidan rediyon Nijeriya Pyramid FM Kano, tare da gurfanar dashi gaban kuliya.
An tuhumi Dahiru da sakin wata hirar sauti da wani dan siyasa a bangaren adawa yana zargin gwamnan da cin hanci da rashawa.
An gurfanar da Dahiru a gaban Kotun Majistare ta 24 a dake Gyadi Gyadi, da laifin bata suna, da kuma cin mutunci.
DCL HAUSA
Advertisements
