Connect with us

News

Juyin Mulki: Rundunar ’Yan Sandan Najeriya Na Neman Ɗan Ƙasar Birtaniya Ruwa A Jallo

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Gwamnatin Najeriya ta ayyana wani dan kasar Birtaniya, Andrew Wynne (Andrew Povich ko Drew Povey), a matsayin wanda take nema ruwa a jallo kan yunkurin kifar da Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Advertisement

Rundunar ’yan Sandan Najeriya ta ce tana gudanar da bincike na musamman kan yadda sojojin sa-kai daga kasar waje suke shiga kasar suna neman hambarar da zababbiyar gwamnatin dimokuradiyya.

Kotu Ta Aike Da Masu Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Zuwa Gidan Yarin Kuje

Mai magana da yawun rundunar, Olumuyiwa Adejobi, ya sanar a ranar Litinin cewa hujjojin da kuma bayanan da suka samu daga Andrew Wynne sun tabbatar da hannunsa a yunkurin kifar da gwamnatin Najeriya.

Advertisement

Adejobi ya bayyana cewa Andrew Wynne ya bayar da tallafin kudade da kuma tsare-tsare zanga-zangar da aka gudanar kan tsadar rayuwa da nufin amfani da zanga-zangar wajen ganin an hambarar da gwamnaitin Najeriya.

Bugu da kari dan kasar na Birtaniya ne ya ba da umarni tare da sanya ido kan zanga-zangar yunwar da aka gudanar a fadin kasar a watan Agusta.

Advertisement

Jami’in ya ce binciken rundunar ya gano cewa Andrew Wynne yana zaman haya ne a gidan Labour House da ke Abuja.

Adejobi, ya ci gaba da cewa Andrew Wynne ya kama wurin haya ne da sunan bude shagon sayar da litattafai mai suna ‘Iva Valley Bookshop’.

Advertisement

Sannan kuma shi ne ya assasa makarantar ‘STARS of Nations Schools’ domin batar da sawu game da manufarsa.

 

Advertisement

 

Aminiya

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending