Connect with us

News

Kamfanin Telekomm Na Fuskantar Barazanar Rufewa Bayan Ma’aikatansa  Sun Fara Yajin Aiki A Najeriya

Published

on

images 5 1

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Kamfanin Sadarwa na Ƙasa, Telekomm Service na fuskantar barazanar rufewa bayan da ƙungiyar manyan jami’an sadarwa da ma’aikatan sadarwa na ƴan kasuwa suka fara yajin aiki.

Advertisement

Ƙungiyar manyan jami’an ta yi gargaɗin samuwar tseko ga harkokin gudanarwar Kamfanin matuƙar ba a amsa buƙatunsu ba.

Ambaliyar Ruwa  Ta Raba Dubban Mutane Da Gidajensu A Maiduguri

Faruwar hakan ka iya jefa miliyoyin masu amfani da ababen sadarwa cikin damuwa a sakamakon rufe kafofinsu.

Advertisement

A ranar Litinin ne aka shiga yajin aikin inda ƙungiyar ta buƙaci a dawo da wasu maaikatanta da aka kora, a ɗaukaka matsayinta, a inganta wajen gudanar da ayyuka da kuma biyan kuɗin mambobi.

A lokacin da ya ke ganawa da manema labarai, babban sakataren ƙungiyar, Okonu Abdullahi ya ce ma’aikatan da suka tafi yajin aikin su na da muhimmiyar rawa da suke takawa wajen gudanar da manyan ayyuka a kamfanoni ciki har da IHS da Huawei da sauransu.

Advertisement

Ya ce, daga cikin su akwai injiniyoyi, injiniyoyin sadarwa, injiniyoyin hulɗa da jama’a, da wasu ma’aikata da ke aiki a kamfanonin Telecom sabis.

A kwanakin baya ne cikin watan Afrilu, ƙungiyar ta shiga irin yajin aikin wanda daga bisani ma’aikatar ƙwadago da kamfanonin sadarwa suka sulhunta lamarin.

Advertisement

Daga ƙarshe, ya ce suna ƙoƙarin shawo kan matsalolin duk da cewa ƙungiyar ta ƙi amincewa ta saurare su.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending