News
Ambaliyar Ruwa Ta Raba Dubban Mutane Da Gidajensu A Maiduguri
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Dubban mutane ne suka yi hijira daga gidajensu a wasu sassan Maiduguri a Jihar Borno da ke Nijeriya sakamakon ambaliyar ruwa.
Bidiyoyin da suka rinƙa yawo a shafukan sada zumunta sun nuna yadda ruwa ya shanye tituna, mutane na guduwa domin neman mafaka.
Adadin Mutane Da Suka Kamu Da Cutar Kyandar Biri A Najeriya Ya Kai 53 — Hukumar NCDC
Ambaliyar ta tilasta wa dubban jama’a kwana a waje sakamakon yadda ambaliya ta shanye musu gidaje.
Ambaliyar wadda ta soma tun a makon da ya gabata, ta yi ƙamari a ranar Litinin da dare, inda aka wayi garin Talata mutane da dama sun shiga cikin wani hali.
Rahotanni sun nuna cewa ambaliyar ta faru ne sakamakon ɓallewar madatsar ruwa ta Alao da ke Ƙaramar Hukumar Konduga a Jihar Borno.
Tun a ranar Litinin gwamnatin ta Borno ta umarci a rufe makarantu a jihar sakamakon take-taken da gwamnatin jihar ta Borno ta gani na yiwuwar ambaliyar ruwan ta ƙara ƙamari.
Sassan Nijeriya na ci gaba da fuskantar ambaliyar ruwa sakamakon mamakon ruwan sama da aka samu, wanda dama tuni hukumar hasashen yanayi ta ƙasar ta yi hasashen samun wannan ambaliya.
Ɗaruruwan mutane ne hukumar bayar da agajin gaggawa ta bayar da rahoton sun rasu a ƙasar sakamakon ambaliyar ruwan, jihohin Bauchi da Sokoto da Zamfara da Jigawa na daga cikin jihohin da ambaliya ta fi yi wa ɓarna a ƙasar.
