News
Kungiyar Likitoci Za Ta Shiga Yajin Aiki A Ranar Samun ’Yancin Kai
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Kungiyar likitocin hakori ta kasa ta sanya ranar 1 ga watan Oktoba a matsayin ranar da mambobinta a Kano za su shiga yajin aikin yayin cikar Najeriya shekara 64 da samun ’yancin kai.
Sakataren kungiyar na Kano Dr. Anas Idris Hassan ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai kamar yanda jaridar NIGERIAN TRACKER ta ruwaito.
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Muta Ne Bakwai A Matsayin Manyan Shuwagabanni Zartarwa
Dokta Anas ya bayyana cewa duk da yarjejeniyar da suka cimma da gwamnatin jihar Kano watannin da suka gabata domin biyan bukatunsu, har yanzu gwamnatin ba ta mayar da martani ba.
Dakta Anas ya ci gaba da cewa, sabbin likitocin da suka dauka aiki, wadanda gwamnatin jihar Kano ta dauka aiki a watan Satumbar 2023, ba a biya su albashi ba.
Likitocin sun kuma nuna damuwarsu kan yadda asibitocin Kano ke tabarbare da kuma karancin kayan aiki, inda suka jaddada bukatar gaggauta magance wadannan matsaloli.
Likitocin sun kara cewa ba su da wani zabi illa shiga yajin aikin a ranar 1 ga Oktoba.
