Sports
Pillars Da Heartland Sun Raba Maki A Filin Wasa Na Sani Abacha.
DAGA UMAR IBRAHIM HOTORO
Kano Pillars ta tashi 2-2 da Heartland a gasar Premier League ta Najeriya da suka kara ranar Lahadi a filin wasa na Sani Abacha da ke Kofar Mata.
Wannan shi ne karon farko da Pillars ta buga wasa a gida tun fara kakar bana, bayan da ta dunga fafatawa a jihar Katsina tun da aka fara kakar nan.
Gwamnatin Tarayya Ta Roƙi Chadi Kada Ta Janye Daga Cikin Ƙasashen Dake Yaƙi Da Boko Haram
Pillars ta zaɓi buga wasanninta a jihar Katsina, sakamakon da aka fara gyaran filin wasa na Sani Abacha da ke kofar mata duk da cewa ba’a ga muciji tsakanin tawagar ta masu gida da kuma katsina united.
Suraju Lawan ne ya fara ci wa Heartland ƙwallo, bayan da suka koma zagaye na biyu daga baya Rabi’u Ali ya warware kallon.
Minti biyu tsakani Heartland ta zura ta biyu a raga ta hannunn Surajo Lawan, wanda yayi nasarar zuwa kwallo biyu a karawar ta hamayya.
Sauran minti 15 a tashi daga fafatawar Pillars tayi nasarar warware kwallon ta hannun babban dan wasanta Ahmed Musa wanda ya bawa kungiyara ta masu gida damar raba maki tsakaninta da kungiyar ta heartland a gaban magoya bayan kungiyar ta kano pillars.
Sakamakon wasannin da aka buga a jiya Lahadi:
Ikorodu City City 2-1 Shooting Stars
Enugu Rangers 3-2 Bendel
Sunshine Stars 1-0 Lobi Stars
Abia Warriors 1-1 Enyimba
Remo Stars 0-0 Rivers Utd
Kwara United 2-0 Plateau Utd
El Kanemi 1-0 Niger Tornadoes
Bayelsa United 1-1 Katsina United
Ranar Asabar 23 ga watan Nuwamba Pillars za ta ziyarci Lobi Stars a wasan mako na 13 a babbar gasar tamaula ta Najeriya.
