Connect with us

News

Kungiyar Miyatti Allah ta kirkiro taron shan fura da nono na Duniya 

Published

on

IMG 20241213 WA0031

DAGA LAWAL ZUBAIRU

Akaron farku kungiyar Fulani ta miyyati Allah Koltol-Hore ta kasa ta kirkiro taron shan fura da nono na Duniya.

Advertisement

Taron da ya gudana ranar Juma’a 13/12/2024 a unguwar Tudun wada dake karamar hukumar Karu cikin jihar Nasarawa.

Shugaba Tinubu  Da Manyan Yan Siyasa Sun Halarci Daurin Auren Ya’yan Sanata Barau Jibril Maliya  

Kungiyar Fulani ta Miyyati Allah karkashin jagorancin Alhaji Bello Bodejo ta gudanar da taron bikin shan fura da Nonon shanu ta duniya tare da nuna al’adun Fulani.

Advertisement

Bayan bude kasuwar Shanu da bude sabon masallaci a Filin maliya aka cigaba da gudanar da taron shan Nono.

Taron da ya samu halartan manyan baki maza da mata da yan kasuwa daga sassa dabam dabam a arewacin Najeriya.

Advertisement

Da yake jawabin a madadin Alhaji Bello Bodejo Shugaban kungiyar na yankin Arewa ta gabas Injiniya Ibrahim Adamu.

Yace; wannan taro uku da aka hadasu waje daya karkashin jagorancin Alhaji Bello Bodejo. An gudanar da taron ne domin cigaban Arewa da qasa baki daya.

Advertisement

Yace; Alhaji Bello Bodejo ya Samar da wannan kasuwar ta sayar da dabbobi badan cigaban kansa ba. Sai dan cigaban Najeriya.

Yace; wannan kasuwar tana yankin Arewa ta tsakiya da ta hada bangarorin kasar baki daya.

Advertisement

Yace; yan kasuwa daga kowani sassa zasu iya haduwa domin hada hadan harkan kasuwanci a kasuwan maliya.

Yace; maliya itace babban kasuwan Dabbobi a kasan nan, a yanzu Wanda zata samar da cigaba mai tarin yawa.

Advertisement

Yace; kuma taron shan Nonon shanu yan nuna cigaban al’adun Fulani an kuma samar da Na’urar tatsan Nonon shanu da zasu iya shayar da al’umman Najeriya miliyoyin litan madara.

Ya kuma bayyana farin cikinsa da shirin Gwamnatin tarayya na kokarin Samar da ma’aikatan kiwon Dabbobi na qasa.

Advertisement

Shima a nasa jawabin Sanata Abdullahi Adamu, Wanda ya samu wakilcin Alhaji Shehu Tukur. Ya yabawa Bello Bodejo da kokarin da yayi na bunkasa kasuwar Dabbobi a wannan yankin ta Arewa.

Yace; Bello Bodejo mutumne da yayi abin bajinta Dan cigaban harkan tattalin arziki a kasa .

Advertisement

Alhaji Shehu Tukur yayi kira ga yan kabilar Fulani dasu zama masu hadin kai da tabbatar da zaman lafiya.

Yace; Allah ya azuta Fulanin Najeriya da arzikin Shanu. Dan haka su zauna lafiya da kowata kabila.

Advertisement

Daga karshe anyi adu’ar Allah ya kwato Shugaban kunhiyar Alhaji Bello Bodejo daga tsare shi da akayi a hannun jami’an tsaro.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending