Connect with us

News

DMCSA Za Ta Hada Hannu Da NDLEA Don Yaki Da Shan Miyagun Kwayoyi A Kano

Published

on

IMG 20241224 WA0009

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Hukumar Samar da Magunguna da Kayan Aikin Asibiti ta Jihar Kano DMCSA ta nemi hadin kan Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa NDLEA reshen Jihar Kano don yakar mummunar ta’adar nan ta ta’ammaali da miyagun kwayoyi, musamman a tsakanin ma’aikatan gwamnati.

Advertisement

Shugaban Hukumar Samar da Magunguna ta Jiha, Famasist Gali Sule ne ya bayyana haka yayin da ya kai ziyarar aiki zuwa Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi da ke nan Kano a safiyar Litinin din nan.

Sai Tsohon Kayan Mu Ya Kare Zamu Rage Farashin Man Fetur — Kungiyar IPMAN

Famasist Gali Sule ya nuna damuwarsa sakamakon yanda shan miyagun kwayoyi ya zama ruwan dare, musamman a tsakanin matasa, a fadin jihar nan.

Advertisement

Shugaban ya ce za su yi wa dukkanin ma’aikatan hukumar, ciki har da shugannin ma’aikatar, gwajin shan miyagun domin tabbatar da da’a.

Haka zalika, hukumar za ta shirya taron wayar da kai a kan illar shan miyagun kwayoyi, in ji shi.

Advertisement

Da yake jawabi, Kwamandan hukumar ta NDLEA reshen jihar Kano Abubakar Idris Ahmad, wanda ya sami wakilcin Mukaddashin Kwamanda Yaya Muhammad Aminu, ya ce ma’aikatarsa a shirye take domin hada kai da Hukumar Samar da Magunguna ta Jihar Kano domin yaki da ta’ammali da miyagun kwayoyi.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending